Wanene Yesu? — Nazarin Baibul na KJV tare da Lambobin Strong — Gwajin Baibul
Gwajin Baibul
Wanene Yesu? — Nazarin Baibul na KJV tare da Lambobin Strong — Gwajin Baibul
Ga kowace ayar da take a ƙasa, zaɓi abin da ayar take koyarwa. Sakamakonka zai bayyana a ƙarshe.
Wannan ita ce jarabawar da za a yi maki. Ka ci ta domin samun ƙima zuwa Takardar Amincewar Hidimarka.
Ishaya 9:6 — Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban ________, Sarkin Salama.
tsufa
budurwa
Madawwami
Farawa 1:26 — Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, ________ sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
garken
al’umma
tsuntsayen
Yohanna 1:18 — Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya ________ shi.
kake
Kana
bayyana
Malaki 3:1 — “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya ________ a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
hanya
ƙauna
dabbobi
Farawa 22:2 — Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka ________, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
Ishaku
Isuwa
Abram
Yohanna 19:17 — Ɗauke da ________, ya kuwa fita zuwa wurin Ƙoƙon Kai (wanda a harshen Arameya ana ce da shi Golgota).
gicciyensa
lauje
fitila
Yohanna 1:29 — Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan ________ na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
Rago
Iblis
haifa
Ishaya 53:6 — Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa ________ da ya wajaba a kanmu.
amincinka
hukuncin
roƙo
Ishaya 53:7 — Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa ________, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
azaba
alkawari
duhu
Ishaya 7:14 — Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi ________ za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
budurwa
harshen
ɗamara
Mika 5:2 — “Amma ke, ________ ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
Yuferites
Damaskus
Betlehem
Farawa 3:15 — Zan kuma sa ƙiyayya tsakaninka da macen, tsakanin ________ da zuriyarta. Zai ragargaje kanka, kai kuma za ka sari ɗiɗɗigensa.”
zuriyarka
albarka
bayyana
Yohanna 1:1 — ________ farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
Tun
dole
fito
Yohanna 1:14 — Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ________ ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
ɗaukaka
ƙauna
bakin
Kolossiyawa 2:9 — Gama a cikin Kiristi cikin jiki dukkan cikar Allahntaka take ________
tabbata
zunubi
hukunta
Yohanna 5:39 — Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai ________. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina
madawwami
ƙarshe
almajirin
Romawa 3:23 — gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ________ Allah
ɗaukakar
ƙauna
fushin
Ibraniyawa 9:22 — Tabbatacce, doka ta bukaci a tsabtacce kusa kowane abu da jini, kuma in ba tare da zub da jini ba babu ________.
gafara
taurin
bambanta
1 Timoti 2:5 — Gama Allah ɗaya ne, ________ kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu
kamunkai
matsakanci
manzo
Ibraniyawa 1:8 — Amma game da Ɗan ya ce, “________, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka.
Kursiyinka
ƙuruciyarka
koyarwa
Zabura 110:1 — Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama ________ sawunka.”
matashin
baiwarka
Fansarki
1 Korintiyawa 15:20 — Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, ________ fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
nunan
ikkilisiyoyi
hatimi
Kolossiyawa 1:27 — Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a ________.
girma
gani
bayyana
Ru'uya ta Yohanna 1:7 — “Duba, yana zuwa cikin ________, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.” Bari yă zama haka nan! Amin.
karnuka
gizagizai
ƙa’idodi
Ayyukan Manzanni 4:12 — Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ________ sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
bishara
bangaskiya
ƙarƙashin
Yohanna 3:16 — Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai ________.
Wannan nazari ya taimaka maka? Raba shaidarka a taƙaice ko cikakke — labarinka zai taimaka wa wani ya samu wannan shafin.
Ajiye ci gabanka
Ba dole ba ne. Ba za ka taɓa buƙatar asusun ba don amfani da wannan shafin.
Ajiye sakamakon jarabawarku da takardar shaidarku ko da kun canza wayarku ko share bayanan burauzarku.
Dawo da ci gaba
Dawo da ci gaba zai maye gurbin ci gaban da ke kan wannan na'ura, kuma duk takardar shaidar da ka buga bayan haka za ta ɗauki sunan da ke cikin rikodin.